Litinin 8 Yuni 2026 - 13:11
An Gudanar Da Gagarumin Taron Bukukuwan Eidul-Ghadeer Cikin Tsari A Faɗin Ƙasar Nijeriya

Hauza/ Sakamakon zagayowar ranar Eidul-Ghadeer Khum, ranar da aka ayyana shugabanci da wilayar Ameerul Mu’uminin Imam Ali bin Abi Dalib (AS), rassan Da’irori na Harkar Musulunci a Nijeriya (almajiran Sayyid Ibraheem Yaqoub Zakzaky) tare da haɗin gwiwar malamai, masana, da mabiya ɗariƙun sufaye da ma sauran al'umma, sun gudanar da gagarumin taro da bukukuwa na musamman a manyan biranen dake Arewacin ƙasar.

A cewar rahoton sashen ƙasa da ƙasa na Kamfanin Dillancin Labaran Hauza, sakamakon zagayowar ranar Eidul-Ghadeer Khum, ranar da aka ayyana shugabanci da wilayar Ameerul Muuminin Imam Ali bin Abi Dalib (AS), rassan Da’irori na Harkar Musulunci a Nijeriya (almajiran Sayyid Ibraheem Yaqoub Zakzaky) tare da haɗin gwiwar malamai, masana, tare da halartar mabiya ɗariƙun sufaye da ma sauran al'umma, sun gudanar da gagarumin taro da bukukuwa na musamman a manyan biranen dake Arewacin da Kudancin ƙasar.

Waɗannan tarurruka da aka gudanar na tsawon kwanaki biyu a jere, sun samu halartar dubban al’umma da suka haɗa da malamai, masana, matasa da iyali, waɗanda suka fito domin nuna muhimmancin wannan rana mai girma.

1. Bayyanar Haɗin Kai A Zuciyar Birnin Kano; Rera Waƙar "Salam Farmande" A Babban Masallacin Juma'a

A ɗaya daga cikin manyan tarurrukan da aka gudanar, harabar babban Masallacin Juma'a na garin Kano da ke fadar Masarautar Kano, ta karɓi bakuncin dubban masoya da mabiya Iyalan gidan Annabi (AS). Wannan taro, wanda shi ne irinsa na farko da aka gudanar da irin wannan babban taro na al'umma a wannan muhimmin waje, an buɗe shi ne da karatun Alkur'ani mai girma daga rukunin "Huffaz Forum" da kuma karatun Ziyarar Amirul Muminin daga rukunin "Shurafa Forum".

A wurin taron, bayan rera waƙoƙin yabo da mawaƙa sanannu suka yi ga Imam Ali (AS) da Sayyada Fatima (AS), daukacin al’ummar da ke wajen sun miƙe tsaye don girmamawa ga Imamul Hujjah (AJ) inda suka rera shahararriyar waƙar nan ta "Farmande" (Salam Farmande) ta yaren Hausa. Haka kuma, ’yan tamsiliyya sun gabatar da wasan kwaikwayo da ke nuna yadda gagarumin al'amarin Ghadeer ya faru a aikace.

Wakilin ’yan’uwa musulmi almajiran Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) na Da’irar Kano da kewaye, Sheikh Dokta Sunusi Abdulkadir, shi ne ya yi jawabi na musamman inda ya bayyana cewa: "Wannan babban taro yana ɗauke da saƙo na musamman ga duniya, ga Nijeriya da kuma garin Kano; mun taru a nan ne domin mu bayyana gaskiyar alƙawarin 'Aliyyun Waliyullah' kamar yadda ya zo a cikin ayoyin Alkur'ani mai girma da ingantattun hadisai. Riko da wilayar Ahlul Baiti (AS) shi ne kaɗai zai kuɓutar da al'umma daga bala'o'in duniya da na lahira."

Taron ya samu halartar wakilin Sarkin Sharifan Kano (Sharif Habibu Zauran Tudu), shugabannin matasan mahaddata Alkur'ani, wakilan makarantu da sauran shugabannin addini da na ɗariƙu.

2. Taron Shekara-Shekara A Garin Zariya Da Kuma Sauraron Jawabin Sayyid Zakzaky

A garin Zariya, wanda shi ne babban birnin ilimi da tarihi, daruruwan masoya wilaya sun taru a harabar makarantar "Fudiyyah" da ke Babban Dodo. A wurin taron, wanda ya sami halartar matasa, manya da tsofaffi, mawaƙa gami da ’yan ɗariƙa sun gabatar da waƙoƙin yabo don nuna haɗin kai da ƙauna ga Imam Ali (AS).

Bayan an gabatar da tamsiliyya (wasan kwaikwayo) mai taken "Cin Amana", wakilin Da'irar Zariya, Sheikh Abdulhamid Bello, ya gabatar da jawabi. Babban abin muhimmanci a wurin taron shi ne sauraro da kuma fashin baki kan sabon jawabin da Jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya, Sayyid Ibraheem Yaqoub Zakzaky (H), ya fitar na musamman domin taron Eidul-Ghadeer na wannan shekara ta 1447 (2026), wanda al'umma suka saurara cikin natsuwa da farin ciki. An kammala taron da yanka alkaki da kuma gudanar da sallolin Magriba da Isha'i.

3. Kayataccen Rufe Bukukuwan Ranar Ghadeer A Jihar Bauchi

Haka kuma, babban ginin Husainiyyah na birnin Bauchi ya karɓi bakuncin taron tattaunawa da bukukuwan ranar Ghadeer na tsawon kwanaki biyu. Taron, wanda Sheikh Ahmad Yusuf Yashi ya jagoranta, ya sami halartar manyan malamai da wakilan gidajen malamai na addini, kamar wakilin Gidan Ƙadiriyya na Bauchi (Prof. Safiyyudden), Gidan Barebari da kuma Shugaban Ashabul Kahfi.

Malamai da masu jawabi sun yi amfani da ingantattun hadisai da ke cikin littattafan Ahlus-Sunnah wajen bayyana saƙon Ghadeer da wasiyyar Manzon Allah (SAWW) a Hajjin Bankwana. Sun jaddada cewa fahimtar saƙon Ghadeer da yin aiki da koyarwar Ahlul Baiti (AS) shi ne babban silar ƙarfafa alaƙa da Annabi (SAWW) da tafiya a kan tafarkin gaskiya da adalci.

A ƙarshe, Sheikh Ahmad Yusuf Yashi ya gode wa al'umma bisa amsa gayyatar wannan gagarumin taro, inda ya yi addu'ar Allah ya tabbatar da zukata a kan tafarkin gaskiya. Mawaƙan "Ittihadush Shu'ara" kuma sun ƙara wa taron armashi ta hanyar rera kasidu na musamman da suka shafi falalar ranar Ghadeer da martabar Imam Ali (AS), wanda hakan ya kawo ƙarshen taron.

An Gudanar Da Gagarumin Taron Bukukuwan Eidul-Ghadeer Cikin Tsari A Faɗin Ƙasar Nijeriya

An Gudanar Da Gagarumin Taron Bukukuwan Eidul-Ghadeer Cikin Tsari A Faɗin Ƙasar Nijeriya

An Gudanar Da Gagarumin Taron Bukukuwan Eidul-Ghadeer Cikin Tsari A Faɗin Ƙasar Nijeriya

An Gudanar Da Gagarumin Taron Bukukuwan Eidul-Ghadeer Cikin Tsari A Faɗin Ƙasar Nijeriya

An Gudanar Da Gagarumin Taron Bukukuwan Eidul-Ghadeer Cikin Tsari A Faɗin Ƙasar Nijeriya

An Gudanar Da Gagarumin Taron Bukukuwan Eidul-Ghadeer Cikin Tsari A Faɗin Ƙasar Nijeriya

An Gudanar Da Gagarumin Taron Bukukuwan Eidul-Ghadeer Cikin Tsari A Faɗin Ƙasar Nijeriya

An Gudanar Da Gagarumin Taron Bukukuwan Eidul-Ghadeer Cikin Tsari A Faɗin Ƙasar Nijeriya

An Gudanar Da Gagarumin Taron Bukukuwan Eidul-Ghadeer Cikin Tsari A Faɗin Ƙasar Nijeriya

An Gudanar Da Gagarumin Taron Bukukuwan Eidul-Ghadeer Cikin Tsari A Faɗin Ƙasar Nijeriya

An Gudanar Da Gagarumin Taron Bukukuwan Eidul-Ghadeer Cikin Tsari A Faɗin Ƙasar Nijeriya

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha